IQNA

Jiragen Yakin Saudiyya Sun Kaddamar Da Hare-Hare A Hudaida

23:59 - December 04, 2018
Lambar Labari: 3483181
Rahotanni daga kasar Yemen sun habarta cewa tun daga jiya har zuwa safiyar yau jiragen yakin Saudiyya kan lartdin Hudaida da ke yamamcin Yemen.

Kamfanin dillancin labaran Sputnik ya bayar da rahoton cewa, da jijjifin safiyar yau jiragen yakin Saudiyya sun kaddamar da munana hare-harea  kan yankin Shari'a Ts'in da ke cikin garin Al-shabab a cikin gundumar Alhudaiadah da ke yammacin kasar Yemen.

Rahoton ya ce a cikin 'yan kwanakin Saudiyya da hadaddiyar daular larabawa da ke mara mata baya a yakin yemen, suna ci gaba da kaddamar da munanan hare-hare a kan birane daban-daban na kasar Yemen.

Wadannan hare-hare dai suna zuwa ne kwana daya kafin fara tattaunawa kan shirin zaman lafiya da sulhu a kasar ta Yemen a karkashin jagorancin majalisar dinkin duniya, wanda Saudiyya take nufin ganin ta rusa hakan ko ta wace hanya.

A nasu bangaren mayakan Ansarullah da aka fi sani da Huthi, da suke mara baya ga sojojin kasar masu yaki da mamayar Saudiyya sun sanar da cewa, an rattaba hannu kan wata yarjejeniyar musayar fursunoni a karkashin jagorancin kungiyar Red Cross.

3769486

 

captcha