Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al Ahed cewa, Sheikh Maher Hammoud shugaban kungiyar malaman gwagwarmaya ta kasa da kasa ya gana tare da tattaunawa da Sayyid Hassan Nasrallah, babban sakataren kungiyar Hizbullah a kasar Lebanon.
A cewar wannan rahoto, a wannan taro an tattauna halin da ake ciki da kuma sabbin abubuwan da ke faruwa a kasar Labanon da kuma yankin.