Babban malami Mufti na Oman ya yi kira ga mahukuntan Indiya da su mutunta hakkin musulmin Indiya, kamar yadda a lokacin mulkin musulmi a kasar wadanda ba musulmi ba, ba su ganin komai sai mutuntawa da adalci daga masu mulki a kasar.
Shafin sadarwa na yanar gizo na Al-Khaleej Online cewa, Sheikh Ahmad bin Hamad Al-Khalili, Mufti na kasar Oman, ya yi Allah wadai da matsin lamba da muzgunawa musulmin Indiya, musamman mata, tare da yin kira da a samar da mafita a kasar.
Al-Khalili ya bayyana cikakken goyon bayansa ga Musulman Indiya a shafinsa na Twitter, yana mai cewa gwamnatin Modi mai tsatsauran ra'ayi a Indiya tana yin abin Allah wadai, musamman cin zarafin dalibai musulmi da aka yi a baya-bayan nan da kuma hana su shiga jami'a saboda sanya hijabi.
Mufti na Oman ya ce: "Labari mai ban tausayi har yanzu yana zuwa mana daga Indiya, masu tsattsauran ra'ayi na can suna samun sabbin abubuwa a kowace rana don muzgunawa da kai wa musulmi hari."
Ya kara da cewa: "A karshe dai an matsa wa mace musulma 'yar kasar Indiya lamba a cikin hijabi na addini, kuma wannan lamari ne da ya shafi cin zarfin addini."
Sheikh Al-Khalil ya ce: "An san cewa kasar Indiya ta shafe shekaru aru-aru da shuwagabannin musulmi suke mulkin kasar, kuma babu wani abu da ake yi face girmama shugabannin sauran addinai a cikin akidarsu da ibadarsu da dukkan al'adunsu."